Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • ijwbq talifi na 29
  • Shin Ya Kamata Na Yi Addu’a ga Waliyai?

Babu bidiyo don wannan zabin

Yi hakuri, bidiyon na da dan matsala

  • Shin Ya Kamata Na Yi Addu’a ga Waliyai?
  • Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
  • Ƙananan Jigo
  • Makamantan Littattafai
  • Amsar Littafi Mai Tsarki
  • Jawowa Kurkusa da Allah Cikin Addu’a
    Menene Allah Yake Bukata a Garemu?
  • Ka Rika Yin Addu’a don Ka Kusaci Allah
    Ka Ji Dadin Rayuwa Har Abada!​—Don Nazarin Littafi Mai Tsarki
  • Gatan da Muke da Shi Na Yin Addu’a
    Me Za Mu Koya Daga Littafi Mai Tsarki?
  • Jehobah Yana Saurarar Mu Kuwa?
    Ka Saurari Allah Don Ka Rayu Har Abada
Dubi Ƙari
Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki
ijwbq talifi na 29

Shin Ya Kamata Na Yi Addu’a ga Waliyai?

Amsar Littafi Mai Tsarki

A’a. Littafi Mai Tsarki ya nuna cewa mu yi addu’a ga Allah kadai kuma a cikin sunan Yesu. Yesu ya gaya wa almajiransa: “Da hakanan fa za ku yi addu’a: Ubanmu wanda ke cikin sama, A tsarkake sunanka.” (Matta 6:9) Bai taba gaya wa almajiransa su yi addu’a ga waliyai ko mala’iku, ko kuma wani ban da Allah ba.

Yesu ya kuma gaya wa mabiyansa: “Ni ne hanya, Ni ne gaskiya, Ni ne rai: ba mai-zuwa wurin Uban sai ta wurina.” (Yohanna 14:6) Yesu ne kadai Allah ya ba wa iznin zama mai roko a madadinmu.—Ibraniyawa 7:25.

Idan na yi addu’a ga Allah da kuma waliyai fa?

A cikin Dokoki Goma, Allah ya ce: “Ni Ubangiji Allahnka Allah mai-kishi ne.” (Fitowa 20:5) Ta yaya Allah “mai-kishi” ne? Hasiya na cikin New American Bible ta ce yana “bukatar biyayya da zuciya daya.” Allah ya bukaci a yi biyayya da sujada da kuma addu’a gare shi kadai.—Ishaya 48:11.

Muna bata wa Allah rai idan muka yi addu’a ga wani, har ma ga waliyai ko mala’iku masu tsarki. Sa’ad da manzo Yohanna ya so ya yi wa mala’ika sujjada, mala’ikan ya hana shi yana cewa: “Kada ka yarda ka yi: ni abokin bauta ne tare da kai da ’yan’uwanka wadanda su ke rike da shaidar Yesu: ka yi sujjada ga Allah.”—Ru’ya ta Yohanna 19:10.

    Littattafan Hausa (1987-2025)
    Fita
    Shiga Ciki
    • Hausa
    • Raba
    • Wadda ka fi so
    • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
    • Ka'idojin Amfani
    • Tsarin Tsare Sirri
    • Saitin Tsare Sirri
    • JW.ORG
    • Shiga Ciki
    Raba