-
Bishiya Mai Cin WutaDarussa daga Littafi Mai Tsarki
-
-
DARASI NA 18
Bishiya Mai Cin Wuta
Musa ya yi shekara 40 a ƙasar Midiya. Ya yi aure kuma ya haifi yara. Wata rana sa’ad da yake kiwon tumakinsa kusa da Dutsen Sinai, sai ya ga wani abin mamaki. Ya ga wata bishiya tana cin wuta amma ba ta ƙone ba. Sa’ad da Musa ya je kusa don ya ga abin da ya sa, sai ya ji wata murya ta ce: ‘Musa! Kada ka zo kusa. Ka cire takalmanka domin kana tsaye a wuri mai tsarki.’ Jehobah ne ya yi amfani da mala’ika don ya yi masa magana.
Musa ya ji tsoro sai ya rufe fuskarsa. Muryar ta ci gaba da cewa: ‘Na ga irin wahalar da Isra’ilawa suke sha. Zan cece su daga ƙasar Masar kuma zan kawo su cikin wata ƙasa mai kyau. Kai ne za ka yi musu ja-gora daga ƙasar Masar.’ Hakan ya ba Musa mamaki, ko ba haka ba?
Musa ya yi tambaya, ya ce: ‘Me zan faɗa idan mutanen suka ce wane ne ya aiko ni?’ Sai Allah ya ce: ‘Ka gaya musu cewa Jehobah, Allahn Ibrahim da Ishaƙu da kuma Yakubu ne ya aiko ka.’ Musa ya ce: ‘Idan mutanen ba su yarda ba fa?’ Sai Jehobah ya yi wani abu da ya sa Musa ya tabbatar da cewa zai taimaka masa. Ya ce Musa ya jefa sandar da ke hannunsa a ƙasa. Sai sandar ta zama maciji. Sa’ad da Musa ya riƙe wutsiyar macijin, sai ya sake zama sanda. Jehobah ya ce: ‘Idan ka yi wannan abin mamaki, za su san cewa ni na aiko ka.’
Musa ya ce: ‘Ban iya magana ba sosai.’ Sai Jehobah ya yi masa alkawari cewa: ‘Zan gaya maka abin da za ka ce, kuma zan sa ɗan’uwanka Haruna ya taimaka maka.’ Da yake Musa ya san cewa Jehobah yana tare da shi, sai shi da matarsa da kuma yaransa suka koma ƙasar Masar.
“Kada hankalinku ya tashi a kan irin magana da za ku yi, ko kuwa abin da za ku faɗi: gama a cikin saʼan nan za a ba ku abin da za ku faɗi.”—Matta 10:19
-
-
Annoba ta Daya Zuwa UkuDarussa daga Littafi Mai Tsarki
-
-
DARASI NA 19
Annoba ta Ɗaya Zuwa Uku
An sa Isra’ilawa su riƙa aiki kamar bayi. Sai Jehobah ya aiki Musa da Haruna su gaya wa Fir’auna cewa: ‘Ka bar mutanena su tafi don su bauta mini a jeji.’ Amma Fir’auna mai fahariya ya ce: ‘Ba ruwana da abin da Jehobah ya faɗa kuma ba zan bar Isra’ilawa su tafi ba.’ Sai Fir’auna ya ce a daɗa wulaƙanta su. Da Jehobah ya ga hakan, sai ya ce zai koya wa Fir’auna hankali. Ta yaya ya yi hakan? Ya kawo Annoba Goma a kan mutanen ƙasar Masar. Sai Jehobah ya gaya wa Musa: ‘Fir’auna yana da taurin kai. Gobe da safe, zai je Kogin Nilu. Ka je wurin ka gaya masa cewa idan bai bar mutanena su tafi ba, duka ruwan Kogin zai zama jini.’ Musa ya je wurin Fir’auna kamar yadda Jehobah ya gaya masa. Fir’auna yana kallo sa’ad da Haruna ya buga ruwan da sandarsa kuma ruwan ya zama jini. Sai ruwan kogin ya soma wari, kifayen da ke ciki suka mutu kuma ba su da ruwan sha. Har yanzu, Fir’auna ya ƙi barin Isra’ilawa su tafi.
Bayan kwana bakwai, sai Jehobah ya ce Musa ya koma wurin Fir’auna kuma ya gaya masa cewa: ‘Zan sa kwaɗi su cika ƙasar Masar idan ba ka bar mutanena su tafi ba.’ Bayan haka, Haruna ya ɗaga sandarsa, sai kwaɗi suka cika ko’ina a ƙasar. An ga kwaɗi a gidaje da kan gado da kuma a cikin kwanuka. Babu inda ba kwaɗi! Sai Fir’auna ya ce Musa ya roƙi Jehobah don kwaɗin su tafi kuma ya ce idan aka yi hakan, zai bar Isra’ilawa su tafi. Sai Jehobah ya kashe kwaɗin kuma mutanen Masar suka kwashe kwaɗi da yawa. Sai gabaki ɗaya ƙasar ta soma wari. Duk da haka, Fir’auna ya ƙi ya bar Isra’ilawa su tafi.
Sai Jehobah ya gaya wa Musa cewa: ‘Ka gaya wa Haruna ya bugi ƙasa da sandarsa kuma ƙasar za ta zama kwarkwata.’ Da ya yi hakan, sai kwarkwata suka cika ko’ina. Wasu daga cikin mutanen Fir’auna sun gaya masa cewa: ‘Wannan annoba ce daga wurin Allah.’ Duk da haka, Fir’auna ya ƙi ya bar Isra’ilawa su tafi.
“Zan sa su san ƙarfina da ikona, za su kuwa sani sunana Yahweh ne.”—Irmiya 16:21, Juyi Mai Fitar da Ma’ana
-