Ƙarin Bayani
a Marubuta na dā, ko kuma Soferim, sun canja wannan ayar ta ce Irmiya ne ba Jehobah ne ya sunkuya ba. Babu shakka suna tunanin cewa bai dace ba a ce Allah ya yi irin wannan tawali’u. Domin wannan, yawancin fassara ba su fahimci batun wannan kyakkyawar aya ba. Amma dai, The New English Bible ya fassara shi daidai Irmiya yana cewa Allah: “Ka tuna, ka tuna, ka sunkuya zuwa gare ni.”