Jumma’a, 12 ga Satumba
Yadda duniyar nan take, tana wucewa ne.—1 Kor. 7:31.
Ku yi abubuwan da za su sa mutane su ga cewa ku masu sanin yakamata ne. Ka tambayi kanka: ‘Shin mutane suna gani na a matsayin mai sanin yakamata? Ba na nacewa a kan raꞌayina kuma ina haƙuri da mutane? Ko dai suna gani na a matsayin mai tsattsauran raꞌayi, marar tausayi kuma mai taurin kai? Ina sauraran mutane kuma in bin shawararsu idan hakan ya dace?’ Yadda muke nuna sanin yakamata zai nuna ko muna yin koyi da Jehobah da Yesu. Muna bukatar mu nuna sanin yakamata idan yanayinmu ya canja. Irin canjin nan zai iya jawo mana matsalolin da ba mu zata ba. Alal misali, za mu iya soma rashin lafiya kwatsam. Faɗuwar tattalin arziki ko kuma wasu canje-canje a gwamnati za su iya sa rayuwa ta yi mana wuya. (M. Wa. 9:11) Ƙari ga haka, zai iya yi mana wuya idan ƙungiyarmu ta canja mana hidima, ko kuma ta ce mu koma yin hidima a wani wuri. Za mu iya jimrewa idan muka bi abubuwa guda huɗun nan: (1) ka amince cewa yanayinka ya canja, (2) ka mai da hankali ga abin da za ka iya yi yanzu ba abin da ka yi a dā ba, (3) ka mai da hankali ga abubuwan da kake morewa yanzu, (4) ka taimaka wa mutane. w23.07 21-22 sakin layi na 7-8
Asabar, 13 ga Satumba
Kai mai daraja ne sosai.—Dan. 9:23.
Annabi Daniyel matashi ne a lokacin da Babiloniyawa suka kama shi suka kai shi zaman bauta a Babila, inda yake da nisa da Urushalima. Babu shakka, Daniyel ya burge su domin sun ga abin da mutum yake gani “daga waje,” wato, Daniyel yana da kyan gani, marar taɓo kuma ya fito daga iyalin da ake darajawa sosai. (1 Sam. 16:7) Waɗannan dalilan ne suka sa Babiloniyawan suka koyar da Daniyel don ya yi hidima a fadar sarki. (Dan. 1:3, 4, 6) Jehobah ya ƙaunaci Daniyel saboda halayensa masu kyau. Mai yiwuwa shekarun Daniyel wajen 20 ne a lokacin da Jehobah ya kwatanta shi da Nuhu da Ayuba. Ko da yake Daniyel matashi ne, a gun Jehobah, shi mai adalci ne kamar Nuhu da Ayuba, waɗanda suka daɗe suna bauta masa da aminci. (Far. 5:32; 6:9, 10; Ayu. 42:16, 17; Ezek. 14:14) Kuma Jehobah ya ci gaba da ƙaunar Daniyel har iyakar rayuwarsa.—Dan. 10:11, 19. w23.08 2 sakin layi na 1-2
Lahadi, 14 ga Satumba
Ku fahimci . . . faɗinta, da tsawonta, da girmanta, da zurfinta.—Afis. 3:18.
Idan kana so ka sayi wani gida, za ka so ka je ka bincika kome da kome game da gidan kafin ka saye shi. Za mu iya bin wannan misalin yayin da muke nazarin Littafi Mai Tsarki. Idan ka karanta Littafi Mai Tsarki cikin hanzari, “koyarwa mai sauƙi ta kalmar Allah” ce kawai za ka fahimta. (Ibran. 5:12) Amma kamar yadda kake bukatar ka shiga cikin gidan da muka ambata, kana bukatar ka yi nazarin Littafi Mai Tsarki da kyau don ka ƙara fahimtar abubuwa da ke ciki. Wani abin da zai taimaka mana sosai shi ne, neman alaƙar da ke tsakanin abin da Littafi Mai Tsarki ya faɗa a wani wuri, da abin da ya faɗa a wani wuri dabam. Ka yi ƙoƙari ka san abubuwan da ka yi imani da su da kuma dalilin da ya sa ka yi imani da su. Don mu ƙara fahimtar abubuwan da ke Littafi Mai Tsarki, muna bukatar mu fahimci koyarwarta masu wuyar fahimta. Manzo Bulus ya shawarci ꞌyanꞌuwansa Kiristoci su yi nazarin Kalmar Allah da kyau domin su ‘fahimci . . . faɗinta, da tsawonta, da girmanta, da zurfinta.’ Yin hakan zai sa su “kafu sosai cikin” bangaskiya. (Afis. 3:14-19) Ya kamata mu ma mu yi hakan. w23.10 18 sakin layi na 1-3