-
“Ka Yi Adalci” Wajen Tafiya da AllahKa Kusaci Jehobah
-
-
13 Idan mun fahimci jinƙai na shari’ar Allah, ba za mu yi hanzarin hukunta wasu ba a al’amuran da ba su shafe mu ba ko kuma waɗanda ba su da muhimmanci sosai. A Huɗubarsa Bisa Dutse, Yesu ya yi gargaɗi: “Kada ku yanke wa kowa hukunci, domin kada a yanke muku.” (Matiyu 7:1) In ji labarin Luka, Yesu ya daɗa cewa: “Kada ku shari’anta kowa, ku kuma ba za a yi muku ba.”a (Luka 6:37) Yesu ya nuna yana sane da cewa mutane ajizai suna da halin hukuntawa. Kowanne cikin masu sauraronsa waɗanda suke da halin hukunta wasu da tsanani ya kamata su daina haka.
Muna nuna shari’a ta Allah sa’ad da muke gaya wa wasu bishara ba tare da son zuciya ba
14. Domin waɗanne dalilai dole mu daina “shari’anta” wasu?
14 Me ya sa za ‘mu daina shari’anta’ wasu? Domin abu ɗaya shi ne, ikonmu yana da iyaka. Almajiri Yakub ya tunasar da mu: “Allah ne kaɗai mai ba da Koyarwa, shi ne kuma mai yin shari’a.” Saboda haka, Yakub ya yi tambayar kai tsaye: “Wane ne kai da har ka isa ka ɗora wa ɗan’uwanka laifi?” (Yakub 4:12; Romawa 14:1-4) Bugu da ƙari, ajizancinmu ba wuya zai sa hukuncinmu ya kasance da kuskure. Halaye da yawa da kuma dalilan da suka sa muka yi haka—haɗe da son zuciya, fahariya, kishi, da kuma adalcin-ƙa—za su iya ɓata yadda muke ɗaukan ’yan’uwanmu mutane. Muna da ƙarin iyaka, kuma yin bimbini bisa waɗannan ya kamata ya hana mu hanzarin kushe wa wasu. Ba ma iya ganin zuciya ba; ba ma kuma iya sanin dukan yanayin wasu ba. To, wanene mu da za mu ɗora wa ’yan’uwanmu masu bi laifi ko kuma mu kushe ƙoƙarinsu a bautar Allah? Ya fi kyau mu yi koyi da Jehobah ta wajen ganin abin da ke nagari cikin ’yan’uwanmu maza da mata maimakon mai da hankali ga kurakuransu!
15. Waɗanne kalmomi ne da kuma bi da mutane ba su da wuri tsakanin masu bauta wa Allah, me ya sa?
15 To, yaya batun hukunta waɗanda suke cikin iyalinmu? Abin baƙin ciki, a duniya ta yau wasu cikin hukunci mafiya tsanani an yi su ne a inda ya kamata ya zama mazaunin salama—gida. Ba abu ba ne mai wuya ka ji game da magidanta azzalumai, mata, da kuma iyaye waɗanda suke yi wa iyalansu “hukuncin” zagi da dūka kullayaumin. Amma, batsa, zagi, da kuma zalunci ba su da waje tsakanin masu bauta wa Allah. (Afisawa 4:29, 31; 5:33; 6:4) Gargaɗin Yesu “kada ku shari’anta” da kuma “kada ku hukunta” bai daina aiki ba yayin da muke gida. Ka tuna cewa yin shari’a ya ƙunshi bi da wasu kamar yadda Jehobah yake bi da mu. Kuma Allah ba ya tsananta mana a hanyar da yake bi da mu. Maimakon haka, yana “yawan tausayi” a kan waɗanda suke ƙaunarsa. (Yakub 5:11) Misali ne mai ban sha’awa da ya kamata mu yi koyi da shi!
-
-
“Ka Yi Adalci” Wajen Tafiya da AllahKa Kusaci Jehobah
-
-
a Fassarar nan “kada ku yanke wa kowa hukunci” da kuma “kada ku shari’anta kowa,” na nufin “kada ku fara yanke” da kuma “kada ku fara shari’anta.” Duk da haka, marubutan Littafi Mai Tsarki sun yi amfani ne da umurni a lamirin lokaci mai ci (mai ci gaba). Saboda haka ayyuka da aka kwatanta na kan faruwa tukuna amma za a daina su.
-