Watchtower LABURARE NA INTANE
Watchtower
LABURARE NA INTANE
Hausa
Ɓ
  • Ā
  • ā
  • Ɓ
  • ɓ
  • ɗ
  • Ɗ
  • Ƙ
  • ƙ
  • ꞌY
  • ꞌy
  • LITTAFI MAI TSARKI
  • WALLAFE-WALLAFE
  • TARO
  • “Kada Ku Sāka Ma Kowane Mutum Mugunta Da Mugunta”
    Hasumiyar Tsaro—2007 | 1 Yuli
    • “Kada Ku Ɗauka Ma Kanku Fansa”

      15. Menene dalilin da ya sa Romawa 12:19 ta ce kada a yi ramuwa?

      15 Bulus ya sake ba da wani dalilin da ya sa bai dace mu yi ramuwa ba; domin hakan ne tafarki mafi kyau da ya kamata mu bi. Ya ce: “Kada ku ɗauka ma kanku fansa, ƙaunatattu, amma ku kauce ma fushi: gama an rubuta, Ɗaukar fansa tawa ce; ni zan yi sakamako, in ji Ubangiji.” (Romawa 12:19) Kirista da ya yi ƙoƙarin yin ramuwa yana da girman kai. Ya ba kansa matsayin da ke na Allah. (Matta 7:1) Ƙari ga haka, ta wajen yin ramuwa da kansa, ya nuna rashin bangaskiya ga tabbacin da Jehobah ya bayar: “Ni zan yi sakamako.” Akasin haka, Kiristoci na gaskiya sun yarda cewa Jehobah zai “rama ma zaɓaɓunsa.” (Luka 18:7, 8; 2 Tassalunikawa 1:6-8) Shi ya sa suka bar ramuwa a hannun Allah.—Irmiya 30:23, 24; Romawa 1:18.

  • “Kada Ku Sāka Ma Kowane Mutum Mugunta Da Mugunta”
    Hasumiyar Tsaro—2007 | 1 Yuli
    • 18. Me ya sa ya dace kuma nuna kauna ce da yin filako idan muka guji ramawa?

      18 A wannan tattaunawar na Romawa sura 12, mun ga dalilai masu muhimmanci da suka sa ba ma “sāka ma kowanne mutum mugunta da mugunta.” Na farko, guje wa ramuwa shi ne tafarkin da ya dace da za mu bi. Saboda juyayin da Allah ya nuna mana, ya dace mu miƙa kanmu ga Jehobah kuma mu bi dokokinsa da son rai, har da dokarsa da ta ce mu ƙaunaci maƙiyanmu. Na biyu, ƙin rama mugunta da mugunta tafarki ne na ƙauna da ya kamata mu bi. Ta wajen son zaman lafiya da kuma ƙin ramuwa, za mu so mu taimaki masu yin hamayya sosai su zama masu bauta wa Jehobah. Na uku, guje wa rama mugunta da mugunta zai nuna cewa muna da filako. Ramawa da kanmu zai nuna cewa muna da girman kai, saboda Jehobah ya ce: “Ni zan yi sakamako.” Kalmar Allah kuma ta yi gargaɗi: “Lokacin da girman kai ya zo, kunya tana nan tafe: Amma wurin masu-tawali’u akwai hikima.” (Misalai 11:2) Barin ramuwa a hannun Allah zai nuna cewa muna da filako.

Littattafan Hausa (1987-2025)
Fita
Shiga Ciki
  • Hausa
  • Raba
  • Wadda ka fi so
  • Copyright © 2025 Watch Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania
  • Ka'idojin Amfani
  • Tsarin Tsare Sirri
  • Saitin Tsare Sirri
  • JW.ORG
  • Shiga Ciki
Raba